Idan kuna biye da shirin, makon da ya gabata muka gabatar maku da daya daga cikin misalan keta hakkin kananan yara da kasashen duniya suka amince zasu dauki matakin karewa, inda a jihar Plateau aka kona wadansu kananan yara bisa zargin maitanci.
Shirin Domin Iyali, ya yi hira da Jeniffer Yerima shugabar kungiyar 'yan jaridu mata reshen jihar Plato , da kuma ta kuma Kachallom Tashio lauya dake bin diddigin wannan batu wadanda suka bayyana yadda suka fara samun labarin da kuma matakan da suke dauka na shawo kan irin wannan matsalar.
Saurari cikakken shirin domin karin bayani.
-
Grace Alheri Abdu
Grace Alheri Abdu babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.