Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutane Tare Da Yin Mummunar Barna A Jihar Filato


Ambaliayr Ruwa Ta Kashe Mutane Hudu, Ta Shafe Gonaki, Gidaje Da Gadoji A Wasu Hukumonin Jihar Filato
Ambaliayr Ruwa Ta Kashe Mutane Hudu, Ta Shafe Gonaki, Gidaje Da Gadoji A Wasu Hukumonin Jihar Filato

Hukumomi a karamar hukumar Pankshin ta Jihar Filato, sun tabbatar da mutuwar mutane hudu, ciki har da wata mace da mijinta, sanadiyyar ambaliyar ruwa da ta auku a kauyukan Nyelleng da Gwabi.

PLATEAU, NIGERIA - Haka kuma a karamar hukumar Quan Pan, ambaliyar ruwa ta shafe gonaki, gidaje da gadoji.

Ambaliayr Ruwa Ta Kashe Mutane Hudu, Ta Shafe Gonaki, Gidaje Da Gadoji A Wasu Hukumonin Jihar Filato
Ambaliayr Ruwa Ta Kashe Mutane Hudu, Ta Shafe Gonaki, Gidaje Da Gadoji A Wasu Hukumonin Jihar Filato

A unguwannin Gangare da Rikkos da ke karamar hukumar Jos ta Arewa ma, ambaliyar ta kwashe gadar da ta hada yankunan biyu, amma tuni shugaban karamar hukumar, Shehu Bala Usman ya sake gina gadar, don hana aukuwar wani ibtila’in.

Tsohon kansila a yankin Nyelleng a karamar hukumar Pankshin, Sudan Bako ya ce karfin ruwa dake saukowa daga tsaunukan dake kewaye da kauyukan, shine ke haddasa ambaliya da lalata gadoji.

Ambaliayr Ruwa Ta Kashe Mutane Hudu, Ta Shafe Gonaki, Gidaje Da Gadoji A Wasu Hukumonin Jihar Filato
Ambaliayr Ruwa Ta Kashe Mutane Hudu, Ta Shafe Gonaki, Gidaje Da Gadoji A Wasu Hukumonin Jihar Filato
Ambaliayr Ruwa Ta Kashe Mutane Hudu, Ta Shafe Gonaki, Gidaje Da Gadoji A Wasu Hukumonin Jihar Filato
Ambaliayr Ruwa Ta Kashe Mutane Hudu, Ta Shafe Gonaki, Gidaje Da Gadoji A Wasu Hukumonin Jihar Filato

Daraktar Hukumar Wayar Da Kan Jama'a Ta Kasa reshen Jihar Filato, Madam Kaneng Pam-Hworo ta ce hukumar na ci gaba da wayar da kan jama’a don su dauki matakan kare kansu daga illar ambaliya.

A Jihar Binuwai ma, fiye da gidaje dari ne ambaliyar ruwa ta shafa, kamar yadda shugaban hukumar bada agajin gaggawa ta Jihar, Emmanuel Shior ya shaida wa manema labarai.

Ambaliayr Ruwa Ta Kashe Mutane Hudu, Ta Shafe Gonaki, Gidaje Da Gadoji A Wasu Hukumonin Jihar Filato
Ambaliayr Ruwa Ta Kashe Mutane Hudu, Ta Shafe Gonaki, Gidaje Da Gadoji A Wasu Hukumonin Jihar Filato
Ambaliayr Ruwa Ta Kashe Mutane Hudu, Ta Shafe Gonaki, Gidaje Da Gadoji A Wasu Hukumonin Jihar Filato
Ambaliayr Ruwa Ta Kashe Mutane Hudu, Ta Shafe Gonaki, Gidaje Da Gadoji A Wasu Hukumonin Jihar Filato

Darakta a ma’aikatar muhalli ta Jahar Filato, Sunda ‘Danbaki ya bukaci jama’a da su rika bin umurnin hukumar yanayi ta kasa.

A kowace shekara dai, Najeriya na asarar makudan kudade, dalilin ambaliyar ruwa, tana kuma shafar lafiyar al’umma da muhalli dake bukatar hukumomi su maida hankali a kai, don rage barnar da ambaliya ke janyowa a kasar.

Saurari cikakken rahoton daga Zainab Babaji:

Ambaliayr Ruwa Ta Kashe Mutane Hudu, Ta Shafe Gonaki, Gidaje Da Gadoji A Wasu Hukumonin Jihar Filato.mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:16 0:00

XS
SM
MD
LG