Gwamnatin shugaban Amurka Donald Trump ta fitar da wasu sabbin manufofi kan yadda za ta rika hulda da kasashen Afirka.
Amurka ta ce ya zama dole bukatunta, su zamanto abu mafi muhimmanci a dangatakarta da Nahiyar ta Afirka.
A yau Alhamis, mai bai wa shugaban Amurka shawara kan harkar tsaro, John Bolton, ya bayyana wadannan manufofi a nan birnin Washington DC.
Bolton ya kara da cewa, za a rika gudanar da huldar kasuwanci tsakanin Amurka da kasashen Afirka, ta yadda bangarorin biyu za su amfana.
A cewar Bolton daga yanzu, Amurkan ba za ta rika ba kasashen Nahiyar ta Afirka tallafi barkatai ba, sannan ba za ta kara daukan nauyin wani aikin soji na wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya, wanda ba ya haifar da wani abin alheri ba.
Za ku iya son wannan ma
-
Janairu 19, 2021
Yau Jajibirin Rantsar Da Sabon Shugaban Amurka Joe Biden
-
Janairu 19, 2021
Tasirin Jihar Pennsylvania A Zaben Shugaban Kasar Amurka
-
Janairu 18, 2021
Joe Biden Na Shirin Gabatar Da Albishir Ga Al’ummar Amurka
-
Janairu 18, 2021
Masu Sharhi Sun Kwatanta Matakan Tsaro A Washington Da Na Tarihi
-
Janairu 17, 2021
Wani Ayarin Baki Masu Kaura Na Dosar Amurka Daga Honduras
Facebook Forum