Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Ta Ba Wasu 'Yan Kamaru Mafaka Ta Wucin Gadi


Tambarin Hukumar Tsaron cikin gidan Amurka
Tambarin Hukumar Tsaron cikin gidan Amurka

Ministan tsaron cikin gida na Amurka ne ya sanar a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma'a cewa a halin yanzu Amurka na ba da matsayin "kariya na wucin gadi" ga 'yan kasar Kamaru da ke zaune a yankinsu. Wannan sanarwar ta haddasa tambayoyi da dama. 

Amurka ta tofa albarkacin bakinta kan rikicin da ake fama da shi a yankunan masu magana da Ingilishi na kudu maso yamma da arewa maso yammacin Kamaru.

Washington ta ba da matsayin kariya ta wucin gadi ga 'yan kasar Kamaru mazauna Amurka indan wannan bayanin ya sanya farin ciki ga mutanen da abin ya shafa kai tsaye.

Ko da yake, masu sharhi irinsu Patient Parfait Ndom, na dasa alamar tambaya game da abin da ya ƙunsa, a cewar mai sharhi kan siyasa a Kamaru Patient Parfait NDOM.

A fahimtar 'yan siyasa da dama, wannan karamcin da Amurka ta yi, wanda ya kamata ya zama abin al'ajabi, hakika wata hanya ce kawai ta matsin lamba don lanƙwasa gwamnatin Kamaru kan batutuwa da dama, musamman matsayinta da ba ta tantance ba kan rikicin Ukraine.

Sai dai mai sharhin siyasar ya ce, sabanin yadda mutum zai yi tunani, wannan sanarwa daga Fadar White House ba za ta yi tasiri a alakar Amurka da Kamaru ba.

Domin kasashen biyu na morar juna a matakai da dama kan batutuwan da suka shafi diflomasiyya da haɗin gwiwar kasashen biyu.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG