WASHINGTON D.C. —
Tawagar ‘yan wasan kwallon kafar Amurka ta mata, ta lashe gasar cin kofin duniya bayan da ta doke Netherland da ci 2-0 a wasan karshe da aka yi a birnin Lyon na kasar Faransa.
Wannan shi ne karo na hudu da kungiyar take lashe kofin na duniya a jeri -babu kakkautawa.
Tawagar ‘yan wasan ta lallasa takwarorinta na nahiyar turai, da suka hada da Sweden, Spain, Faransa da Ingila kafin su kai wasan karshen, suka kuma doke Netherland, wacce ita ce zakarar nahiyar.
Fitacciyar ‘yar wasan tawagar, Megan Rapinoe ce ta budewa Amurka kofar zura kwallaye bayan da ta yi nasarar buga penarti a minit na 61.
Sannan sai ‘yar wasa Rose Lavelle ta kara wata kwallo ta biyu a minti na 69, aka kuma tashi a haka.
Za ku iya son wannan ma
-
Janairu 25, 2023
Mawakiya Yar Najeriya Ta Yi Tarihi A Bikin Bada Lambar Yabo Na Oscar
-
Janairu 13, 2023
Lisa Marie Presley, Diyar Mawaki Elvis Ta Rasu
-
Janairu 11, 2023
Ana Tsaftace Yankunan Da Mahaukaciyar Guguwa Ta Ratsa A California