Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Za Ta Ba Najeriya Da Wasu Kasashen Afirka Tallafin Dala Miliyan 533


Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Rex Tillerson a Jami'ar George Mason inda ya ke tattaunawa kan dangantakar Afirka Da Amurka gabanin tafiyarsa zuwa nahiyar.
Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Rex Tillerson a Jami'ar George Mason inda ya ke tattaunawa kan dangantakar Afirka Da Amurka gabanin tafiyarsa zuwa nahiyar.

A wani bangare na shirye-shiyensa na kai ziyara nahiyar Afirka, Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Rex Tillserson, ya zayyana irin taimakon da Amurka za ta dada ba wa kasashen Afurka. A baya ya jaddada muhimmancin huldar diflomasiyya da kasuwanci da tattalin arziki da tsaro tsakanin Amurka da Afirka.

Amurka ta ce za ta bayar da tallafin dala miliyan dari biyar da talatin da uku (533 miliyan) ga kasashen Afirka kamar Najeriya, da Habasha, da Somaliya, da Sudan Ta Kudu da kuma kasashen da ke yankin Tabkin Chadi, wato kasashen da ke fama da karancin abinci sakamakon rikici ko suka yi fama da fari na tsawon lokaci.

Sakataren Harkokin wajen Amurka, Rex Tillerson ne ya yi wannan sanarwar yau a Jihar Virginia gabanin ziyarar da zai kai wasu kasashen Afirka guda biyar, ciki har da Najeriya.

Wannan karin kudaden tallafin daga Amurka zai taimaka wajen samar da agajin abinci ga masu bukata, da samar da tsaftataccen ruwan sha, da agajin gaggawa na kiwon lafiya musamman ta wajen dakile cututtuka masu yaduwa a cikin al’umma da sauransu.

A cewar ma’aikatar harkokin wajen Amurka, wadannan kudaden tallafin za a rarraba su kamar haka: Sudan ta kudu za ta samu kusan dala miliyan 184, Habasha da Somaliya kowanensu zai samu sama da dala miliyan 110, sannan kuma dala miliyan 128 zai je ga Najeriya da sauran kasashen da ke yankin tafkin Chadi.

Amurka ta kasance kasar da fi kowacce bayar da taimakon agaji ga kasashen Afirka masu fama da rikici, inda tun daga farkon shekarar 2017 ta bayar da kusan dala biliyan uku.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG