Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka Za Ta Janye Daga Yarjejeniyar Makamai Da Ta Kulla Da Rasha


Shugaban Rasha, Vladimir Putin (Hagu) shugaba Trump, (Dama)

A cewar Trump, Rasha ta jima tana kera makamai masu linzami da aka haramta, wadanda ke zama barazana ga kawayen Amurka da dakarunta da ke kasashen waje.

Amurka ta aikewa da Rasha sakon gargadi, kan cewa za ta janye daga matsayar da aka cimma ta takaita kera madashin makaman nukiliya da na masu linzami.

A jiya Juma’a shugaba Trump ya bayyana cewa, Amurka za ta janye daga wannan matsaya, wacce aka kwashe gomman shekaru da rattaba hannun akanta, inda ta zargi hukumomin Kremlin da take matsayar.

A cewar Trump, Rasha ta jima tana kera makamai masu linzami da aka haramta, wadanda ke zama barazana ga kawayen Amurka da dakarunta da ke kasashen waje.

Sai dai, hukumomin Rashan sun yi maza sun musanta ikrarin na Amurka, suna masu cewa, Amurka na neman hanyar ne kawai, da za ta fadada rumbun makamanta masu linzami.

Facebook Forum

An Sami Karuwar Farashin Kayayyaki A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:42 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shiye-Shiryen Shiga Watan Azumi A Kasar Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:56 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Ziyarar Sakatare Blinken A Jamhuriyar Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Al'umomi Sun Koka Game Da Tashin Farashin Kayayyaki
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:57 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG