Amurka za ta yi amfani da wani sabon salo a kafar labarai, wajen mai da martani kan farfagandar da Rasha ke bazawa, inda Amurka za ta yi amfani da labaran gaskiya da zummar dakile labaran karya da Rasha ke yadawa, a cewar babban Shugaban Hukumar Yada Labaran Gwamnatin Amurka, John Lansing ga wani kwamitin Majalisar Dattawa.
Lansing ya fadi jiya Alhamis cewa ya ga abin da ya kira, "karuwar farfaganda da karerayi a duniya," sannan ya ce a yanzu haka cibiyar gwamnati wadda ya ke jagoranta, ta dukufa wajen dakile irin wadannan karerayin ta wajen amfani da gaskiya. BBG ce hukumar da ke kula da Muryar Amurka da sauran kafofin yada labaran gwamnatin Amurka.
Lansing ya bayyana cikakken matakin da hukumar ta BBG ke daukawa, da zummar dakile karyar da Rasha ke yadawa ta wajen tarar abubuwan da Rashawan ke fadi a sassan duniya.
Kwamitocin bincike dabam-dabam na bin diddigin yinkurin Rasha na yin katsalandan a zaben Shugaban kasar Amurka na 2016 da kuma zabukan da aka yi a Turai.
Amurka Za Ta Wargaza Farfagandar Rasha
- Ibrahim Garba

Ganin yadda Rasha ke ta yada farfaganda a sassan duniya, Muryar Amurka ta lashi takobin wofinta farfagandar
WASHINGTON D.C. —
Za ku iya son wannan ma
-
Afrilu 09, 2021
Mawakin Gambara DMX Ya Mutu
-
Afrilu 09, 2021
Dan Najeriya Da Ya Zama Kyaftin Din Jirgin Yakin Ruwan Amurka
-
Afrilu 03, 2021
An Kashe Wani Dan Sandan Ginin Majalisar Dokokin Amurka
-
Maris 31, 2021
Kakar Barack Obama Ta Rasu
Facebook Forum