Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Gano Wasu Manyan Kaburbura Da Kungiyar IS Ta Binne Mutane


A cigaba da gano wasu abubuwan tayar da hankali da kungiyar IS ta gudu ta bari, a baya bayan nan an gano wasu manyan kaburbura.

Yayin da hukumomi a arewa maso gabashin Syria suka sanar da gano wasu sabbin ramuka da aka jibge gawarwakin wadanda fadan yan kungiyar IS ya shafa a birnin Raqqa, iyalan wadanda ‘yan uwansu suka bace a lokacin da kungiyar ke rike da ikon yankin na fatan samun bayanai.

Tawagar ma’aikatan gaggawa, da na ceton rai a arewa maso gabashin Syria, a farkon watan nan suka sanar da cewa sun gano wani babban rami da aka binne mutane a yamma da wajen yankin Farusiya da ke Raqqa, abinda ya sa yawan irin wadannan wuraren da aka gano a wannan shekarar ya kai 5.

Biyo bayan sanarwar da kuma gano gawarwaki 16 daga ramin, iyalan wadanda lamarin ya shafa sun bukaci hukumomi su maida hankali wajen tantance gawarwakin mutanen.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG