Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Gudanar Da Taron Mabanbantan Addinai a Jos


Mai martaba Sarkin Musulmi, Sa’ad Abubakar ya jaddada cewa duk wadanda ke daukan makami suna kisan jama’a da sunan addini, zasu fuskanci mummunan hukunci daga Allah.

Sarkin na Musulmi da Shugaban kungiyar hadin kan mabiya addinin kirista da suke shugabantar kungiyar dake sasanta tsakanin mabambantan addinai a Najeriya sun je Jos, fadar jahar Filato ne don yin jaje wa al’ummar jahar kan rikicin da ya rutsa da rayukan jama’a da dama a wassu sassan jahar.

Mai martaba ya nanata cewa idan har gwamnati bata dauki matakin hukunta wadanda ke da laifi ba, to lallai zasu ci gaba da kisan mutane da basu ji ba basu gani ba.

Shugaban kungiyar CAN, Samson Olasupo yace burinsu shine tabbatar da zaman lafiya da hada kan jama’a.

Sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha yace gwamnati zata yi adalci wajen gurfanadda masu laifi a gaban kuliya su fuskanci hukunci.

Saurari cikakken rahoton cikin sauti:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:36 0:00

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG