Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Gudanar Da Zabe Mai Inganci A Jamhuriyar Nijar - CEN-SAD


Masu Aikin Sa Ido a Zaben Nijar Daga Kasashen Afirka.
Masu Aikin Sa Ido a Zaben Nijar Daga Kasashen Afirka.

An bayyana zaben shugaban kasar da aka gudanar a Jamhuriyar Nijar a matsayin abin koyi.

Kungiyar kasashen da ke yankin Sahel CEN-SAD, ta nuna gamsuwarta dangane da yadda aka gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokoki a Jamhuriyar Nijar cikin lumana, tana mai kira ga al’umar kasar da su nuna goyon bayan ga shugaban da ya samu nasarar wannan zabe.

Kungiyar ta yi kira ga jam'iyun siyasa da sauran daidaikun al'umma cewa, duk wanda ke da korafi kan zaben, ya bi hanyar da doka ta tanada domin a bi masa kadinsa.

A cikin hirar shi da wakilin Muryar Amurka Souley Moumouni Barma,daya daga cikin jagororin kungiyar Sanata Lawal Gana Guba, ya yi bayani kan yadda kungiyar ta CEN-SAD ta kalli zaben.

Zaben Nijer
Zaben Nijer

Sanata ya ce, sun shaida kayan zabe sun isa akan kari, sun shaida akan samar da jami'an tsaro a duk runfunan zabe, sun kuma shaida cewar mutanen kasar sun yi gagarumin fita runfunan zabe kdon kada kuri'unsu.

Ya bayyana gamsuwa tare da cewa. zaben ya bada mamaki ga duk wanda ya gani, domin kuwa ba a shiga hakkin 'yan kasa ba, babu wata takura, an kuma gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da lumana.

Zaben Nijer
Zaben Nijer

Kungiyar ta bada shawara ga duk 'yan takara akan sakamakon zabe. Sanata Lawal Gana Guba ya ce, "Abu na farko sai anyi hakuri, kana abu da kawai ake bukatar duk wanda yake da ja akan sakamakon zaben, to ya garzaya kotu, domin kuwa akwai dokoki da suka tanaji yadda mutane zasu kalubalanci zabe, babu bukatar a tada hankali."

Saurarri cikakken tattaunawar a cikin sauti.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:59 0:00

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

XS
SM
MD
LG