Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kafa Dokar Hana Yawon Dare A Jihar Adamawa


Hukumomin soja sun ce an haramta ma jama'a fita waje daga karfe 6 na maraice zuwa karfe shida na safiya a dukkan yankunan kananan hukumomin jihar

Hukumomin soja a Jihar Adamawa, a yankin arewa maso gabashin Najeriya, sun ayyana kafa dokar hana fita waje daga karfe 6 na maraice zuwa karfe 6 na safiya a dukkan yankunan kananan hukumomin dake jihar.

Wannan dokar hana fitar zata fara aiki daga yau laraba, 16 ga watan Mayu.

Kakakin birged ta 23 ta sojojin Najeriya a Yola, Leftana Jaafar Mohammed Nuhu, shine ya bayyana wannan a lokacin da yake bayani ga 'yan jarida na irin matakan da suka fara dauka dangane da dokar-ta-bacin da gwamnatin tarayya ta kafa a wasu jihohi uku na yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Leftana Jaafar Nuhu ya bukcai jama'a da su bi doka, su kuma yi aiki da dukkan umurnin da hukumomi zasu bayar domin a samu nasarar maido da zaman lafiya cikin kankanin lokaci.

A halin da ake ciki kuma, kungiyoyin al'umma a Jihar Adamawa sun fara gangamin fadakar da jama'a irin matakan da ya kamata su dauka domin tabbatar da cewa ba su cutu ba a karkashin wannan dokar ta bacin.

Ibrahim Abdulaziz ya aiko da cikakken bayani game da wadannan matakai na hukuma, da abubuwan da kungiyoyin al'umma keyi da kuma ra'ayoyin da jama'a suke bayyanawa na halin da suka samu kansu ciki.

Rahoton Ibrahim Abdulaziz Daga Yola Kan Kafa Dokar Hana Yawon Dare A Jihar Adamawa - 3:06
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:06 0:00
Shiga Kai Tsaye
Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG