Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kafa Dokar Hana Zirga-Zirga A Jihar Edo


Gwamnan Jihar EDO: Godwin Obaseki.
Gwamnan Jihar EDO: Godwin Obaseki.

An sanya dokar hana zirga-zirga a jihar Edo, biyo bayan zanga-zanga da ta kai ga asarar dukiyoyi.

Gwamnatin jihar Edo a Najeriya ta sanya dokar hana zirga-zirga na sa’o’i 24 a yau daga karfe 4 na yamma, har sai baba ta gani a jihar.

A wata sanarwa, sakataren gwamnati jihar Osarodio Ogie ya ce matakin ya zama dole, biyo bayan ayyukan tashin hankali a kan jama'a, da ofisoshin gwamnati a jihar, da wasu ‘yan tada-zaune tsaye suke yi da sunan kawo karshen rundunar SARS.

"Duk kuwa da cewar gwamnatin jihar na goyon bayan ‘yan kasa su gudanar da zanga-zangar lumana, amma wannan ba zai zama dalili da zai sa gwamnati ta zura ido ana cin zarafin wasu ba" a cewar Ogie.

Ya kara da cewa gwamnati ba za ta bari wasu tsiraru su rinka daukar doka a hannunsu ba.

Dokar ta umurci a rufe makarantu, kasuwanni, sannan jama’a da suke cikin zullumi sai su nemi mafaka.

Ya ce ana bukatar iyaye su ja kunnen ‘ya’yansu, a kan bin doka da oda, da mutunta dokar zama a gida.

"Hakki ne da ya rataya a kan gwamnati na kare jama’a da dukiyoyin su, kana da tabbatar da an bi doka da oda, don haka duk wanda aka samu a waje ya karya dokar, za’a hukunta shi dai-dai da tanadin doka", a cewar sanarwar.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG