Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kai Hari A Birnin Diffa Dake Jumhuriyar Niger.


Sojojin Cadi da Nijar sun kashe 'yan Boko Haram, Maris 19, 2015
Sojojin Cadi da Nijar sun kashe 'yan Boko Haram, Maris 19, 2015

Wasu mutanen da ake tuhuma yan boko haram ne sun kai hari a garin Diffa dake cikin jamhuriyar Niger, kuma wani wanda bai so a bayyana sunan sa ba, yayi wa wakilin sashen sashen Hausa Yusuf Abdullahi Karin bayani yadda abin ya faru.

‘’Da musalin karfe bakwai da rabi zuwa wurin takwas da yan muntuna ne wasu yan kunar bakin wake su 4 suka rabu kasha biyu wasu suka nufi cikin gari wasu kuma suka nufi barikin soja.’’

Sun tafi barikin ne da niyyar zuwa gidan shugaban sojojin kasar, suna cikin tafiya ne sai wani dan gari ya gansu sai ya nuna su ga sojan dake gadi kofar gidan babban sojan da suka je gidan nasa.

Shine sai yace ma sojan ga wadansu can wadanda bai yadda dasu ba, a lokacin ne sai sojan ya ,matso kusa dasu, yana tambayar su. Yana kokarin binciken su.

To da aka tambaye shi ko ina ne suka kai harin

Sai yace jitan tara ne.

Ga dai Yusuf Abdullahi Yusuf da Karin bayani ‘2 44’’

An Kai Hari A Birnin Diffa Dake Jumhuriyar Niger. '2 44''

XS
SM
MD
LG