Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kashe Akalla Mutane 15 A Syria,A Farmaki Da Jami'an Tsaro Suka Kai Kan 'Yan Zanga Zanga

Tayoyi da masu zanga zangar nuna kin jinin gwamnati suke konawa,a da wasu shara kan tituna,bayan arangama d a jami'an tsaro.
Tayoyi da masu zanga zangar nuna kin jinin gwamnati suke konawa,a da wasu shara kan tituna,bayan arangama d a jami'an tsaro.

Masu hankoron kare hakkin jama’a a kasar Syria sunce an kashe akalla mutane goma sha biyar a jiya Laraba a birnin Daraa, ciki harda akalla mutane shidda wadanda aka kashe a lokacinda jami’an tsaro suka bude wuta akan masu zanga zangar kin jinin gwamnati kusa da Masallaci.

Masu hankoron kare hakkin jama’a a kasar Syria,sunce an kashe akalla mutane goma sha biyar a jiya Laraba a birnin Daraa, ciki harda akalla mutane shidda wadanda aka kashe a lokacinda jami’an tsaro suka bude wuta akan masu zanga zangar kin jinin gwamnati kusa da a kusa da Masallaci.

Shedun gani da ido sunce akwai akalla yaro daya a cikin wadanda aka kashe. Haka kuma an bada rahoto cewa jami’an tsaro sun kashe karin mutane a jiya Laraban.

To amma ita gwamnatin Syria cewa tayi mutane hudu ne aka kashe a tarzomar ta jiya Laraba. Kamfanin dilancin labarun kasar da ake cewa SANA ya bada labarin cewa mutane hudun da aka kashe a Daraa jami’an kiwon lafiya ne, wadanda yan banga dauke da makamai, suka kai musu hari.

A jiya Laraba ma’aikatar harkokin wajen Faransa tayi Allah wadai da tarzoma a Syria kuma tayi kira ga gwamnatin kasar data kaddamar da sauye sauyen harkokin siyasa.

A ranar talata shugaba Bashar al Assad ya kori gwamnan lardin Daraa. To amma korar gwamnan bata sa masu zanga zanga sun saduda ba.

This item is part of
XS
SM
MD
LG