Wannan harin ya haifar da zaman dar-dar tsakanin al’ummar Arewa dake zaune a jihar ta Bayelsa wadanda suka nemi kariyar jami’an tsaro. Wannan al’amrin ya kuma ya kai ga suka rufe hanyoyin mota domin bayyana damuwarsu ga harin.
Hukumomin tsaro a jihar Bayelsa sun yi alkawari ga al’ummar Arewacin Najeriya dake zaune a jihar cewa za a basu tsaro da dukiyoyinsu. A cewar wani makarabin wadanda aka kaiwa harin, sakataren gwamnatin jihar Bayelsa yace musu kada wani Bauhashe ya ji tsoron gudanar da harkokinsa saboda za a basu cikakken tsaro.
Mai Magana da yawun yan sandan jihar DSP Andrew Busuwad ya bayyana yanda maharan suka kai farmaki a cikin wata mota kirar Mazda. Sai dai yace tuni ma’aikatar yan sandan jihar ta umarci jami’anta su nemi motar su kama ta.
Facebook Forum