Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Kashe Wani Sojan Amurka Na Musamman A Somaliya


Sojojin Somaliya a wani wuri da aka tada bom
Sojojin Somaliya a wani wuri da aka tada bom

An kashe wani sojan amurka na musamman, yayinda aka kuma jiwa wadansu hudu rauni lokacin da kungiyar da ake alakantawa da al-qaida ta kai hari jiya Jumma’a a wani wuri da ake gina karamin sansanin soji a kudu maso yammacin kasar Somalia.

An kai harin jiya jumma’a a wurin dake tazarar kilomita hamsin da birnin Kismayo ne yayinda dakarun Amurka ke taimakawa takwarorinsu na kasashen Somalia da Kenya gina karamin sansani, daga cikin ayyukan da rundunar sojin ke gudanarwa na kakkabe mayaka da kungiyar ta’ddanci ta al-Shabab daga yankin, bisa ga cewar jami’an rundunar sojin Amurka.

Shaidu sun ce an kai harin ne kusa da garin Sangumi, lokacin da dakarun Amurka da Somaliya da kuma Kenya suke gina ramukan shingen kariya suna kuma kakkafa wadansu hanyoyin kariya.

Suka ce mayakan sun fara da jefa nakiyoyi kafin suka bude wuta kan dakarun.

An tura jirgin helicopta domin daukar wadanda suka ji rauni.

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG