Majalisar Dinkin Duniya da kuma kungiyar hadin kan Afrika sun ce, tattaunawa a Khartoum ta kai ga kulla yarjajjeniyar zaman lafiya tsakanin Jamhuriyar Tsakiyar Afirka da kungiyoyi 14 masu dauke da makamai.
Wannan wani abin farin ciki ne da ake kuma fatan alama ce cewa zaman tafiya na tafe bayan tashin hankali na shekaru da dama da kasar ta fuskanta.
Wannan wata rana ce mai matukar muhimmanci ga Jamhuriyar Tsakiyar Afrikan da kuma mutananta gaba daya, a cewar Smail Chergui, kwamishina a kungiyar hadin kan Afrika akan zaman lafiya da tsaro.
Sai dai ba a bayyana sharuddan yarjajeniyar zaman lafiyar nan da nan ba.
Mai Magana da yawun FPRC, daya daga cikin kungiyoyin, Abakar Sabom, ya ce, "mun yadda kan abin da yake da muhimmanci ga kasar Jamhuriyar Tsakiyar Afrika, wato zaman lafiya.”
Sai dai an taba makamanciyar wannan yarjejeniyar a shekarun baya amma ta wargaje.
Za ku iya son wannan ma
-
Janairu 27, 2023
An Samu Take Hakkin Dan Adam Da Dama a Jamhuriyar Nijar - Rahoto
-
Janairu 25, 2023
Ma’aikatan Kasar Nijar Sun Fara Yajin Aiki Na Wuni Biyu
-
Janairu 25, 2023
Dalilin Da Yasa Amurkawa Bakaken Fata Ke Kaura Zuwa Ghana
Facebook Forum