Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Mika Wa Majalisa Sunayen Sababbin Ministoci


Sanata Bukola Saraki, sabon shugaban Majalisar Dattijai, Yuni 9, 2015.
Sanata Bukola Saraki, sabon shugaban Majalisar Dattijai, Yuni 9, 2015.

A yau ne shugaban majalisar dattijan Najeriya ya bayyana cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya aika ma majalisa da jerin sunayen mutanen da ake sa ran zasu zama ministoci.

'Yan Najeriya sun dade suna ta cece kuce dangane da rashin fitar da sunayen ministocin da wuri, lamarin wanda wasu da dama ke ganin wani tsaiko ne ga ci gaban sabuwar gwamnatin, yayin da wasu kuma ke ganin cewa ko da babu minstocin gwamnatin na iya gudanar da ayyukan ta ba tare da wata matasala ba.

Ana sa ran da zarar an bayyana sunayen sababbin ministocin za su fara aiki ba tare da bata lokaci ba.

XS
SM
MD
LG