Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Sace Turawa Biyu A Birnin Kebbi


Sojoji masu gadin rumfar zabe lokacin zaben gwamna a kaduna ranar 28 Afrilu, 2011.
Sojoji masu gadin rumfar zabe lokacin zaben gwamna a kaduna ranar 28 Afrilu, 2011.

Hukumomin 'yan sandan Najeriya sun ce wasu 'yan bindiga sun sace dan Britaniya da dan Italiya daga gidansu a Jihar Kebbi daren alhamisa.

‘Yan sanda a Najeriya sun ce wasu ‘yan bindiga sun sace wani dan Britaniya da wani dan Italiya daga gidan da suke zaune ciki a Jihar Kebbi dake arewa maso yammacin Najeriya.

Jami’ai suka ce an harbi mutum na uku aka ji masa rauni a lokacin da yayi kokarin hana satar wadannan mutanen ranar alhamis da daddare a Birnin Kebbi, babban birnin Jihar.

‘Yan sanda suka ce mutanen biyu da aka sace ma’aikata ne na wani kamfanin gine-gine. Suka ce babu wanda ya aika da takardar neman fansa domin sako mutanen.

An saba da ganin sace-sacen mutane a yankin Niger Delta mai arzikin man fetur a kudancin Najeriya, amma irin wannan al’amari ba sabam-ba ne a yankin arewacin Najeriya.

A makwabciyar Najeriya daga arewa ma, watau Jamhuriyar Nijar, an sha sace ‘yan kasashen waje cikin ‘yan shekarun nan. Jihar ta Kebbi tana iyaka da Jamhuriyar Nijar da kuma Benin.

XS
SM
MD
LG