Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Samu Karin Mace-Mace A Wani Hari Da Aka Kai A Sokoto


Wasu da ake zargin 'yan bindiga barayin Shanu a jihar Zamfara
Wasu da ake zargin 'yan bindiga barayin Shanu a jihar Zamfara

An kashe mutane sama da 48 a harin da wasu masu bindigogi suka kai a kananan hukumomin da ke jihar Zamfara, Katsina da Jamhuriyar Nijer tsaka nin jiya da yau.

Kauyuka 4 ne lamarin ya shafa, da suka hada da Rakonni, Tsagi, da Kalhu da kuma Gi’ire, duk a cikin gundumar Gandi da ke karamar hukumar mulki Tarabah, inda ‘yan bindigar da ba’a gane adadinsu ba.

Masu bindigogin dai, sun fara kashe mutane 18 ne ranar Asabar da ta wuce, sai kuma jiya lokacin da a ke jana'izarsu, suka dawo suka sake bude wuta a kan jama'a, inda mutum 4 suka rasa ra'ikunsu.

Wakilin Muryar Amurka ya ce kananan hukumomin da ke Zamfara, sun dade suna cikin wannan al'amarin kai hari daga 'yan bindigan, kuma sun dauka abin ya lafa, amma sai kuma suka sake samun hari wanda har ya shafi sauran hukumomin da ke kusa da su.

Yanzu haka ana zaman dardar a garuruwa da dama a yankin gabashin jihar Sokoto saboda fargabar kai hari a kowane lokaci, yayin da wasu al’ummomi da dama suka bar garuruwansu.

Ga cikkaken rohoton wakilin Muryar Amurka Murtala Faruq Sayinna

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:50 0:00

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG