Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar NEMA Ta Bayyana Yawan Mutanen Da Suka Mutu a Harin Garin Mubi

Yayin da alkaluman mutanen da suka mutu a tagwayen harin kunar bakin wake da aka kai garin Mubi ke karuwa, yanzu haka an garzaya da wadanda ke da munanan raunuka zuwa cibiyar lafiya dake fadar jihar wato FMC Yola.

Alkaluman da hukumar bada agajin gaggawa ta bada a yau Laraba, hukumar ta ce adadin wadanda suka mutu a wannan tagwayen harin kunar bakin wanken sun karu zuwa mutum 30, baya ga wadanda aka garzaya da su zuwa cibiyar kiwon lafiya ta gwamnatin tarayya, wato FMC Yola.

Domin Kari

XS
SM
MD
LG