Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Samu Rarrabar Kawuna Tsakanin Fulani A Siyasar Jihar Taraba


Gwamnan Jihar Taraba Arch Dickson Isyaku
Gwamnan Jihar Taraba Arch Dickson Isyaku

An sun rarrabuwar kawuna a hadakar kungiyoyin makiyaya a jihar Taraba dake arewa maso gabashin Najeriya,inda a karon farko wasu kungiyoyin makiyaya suka ce sun yafewa gwamnatin jihar tare da bayyana goyon bayansu ga jam’iyar PDP a zabe mai zuwa, yayin da wasu kungiyoyin kuma ke cewa ba zata sabu ba.

Wannan ne karon farko tun bayan dambarwar kafa dokar hana kiwo da gwamnatin jihar Taraban ta kaddamar da gwamnan jihar Arc.Darius Dickson Isiyaku ke samun maslaha da hadakar kungiyoyin makiyaya, inda makiyayan suka mika mubaya'arsu ga gwamnatin PDP a jihar.

Mafindi Umaru Danburam dake zama shugaban kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah mai kula da jihohin arewa maso gabas da ya jagoranci kungiyoyin makiyayan zuwa gwamnatin jihar yace su sun yafe duk abubuwa da suka faru a baya.

A bangarensa kuma, gwamnan jihar Taraban Akitet Darius Dickson Isiyaku ya karyata zargin cewa gwamnatinsa na nunawa musu wariya.

Sai dai kuma yayin da wannan ke faruwa wasu kungiyoyin Fulani sun ce bada yawunsu aka je gidan gwamnatin ba, un kuma ce jam'iyar APC zasu bi. Sahabi Mahmud shine shugaban kungiyar miyetti Allah a jihar ya jagoranci wani taron manema labarai inda suka bayyana matsayinsu da cewa su APC zasu yi ba wata jam’iya ba.

Ga rahoton Ibrahmim Abdulaziz a kan wannan batu daga jihar Taraba:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:54 0:00

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG