Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Samu Takon Saka Tsakanin'Yan jarida Da Jamian Tsaro A Jamhuriyar Niger


'Yan jarida a jamhuriyar Niger sun koka akan yadda jamian tsaro ke takura musu a lokacin da suke gudanar da ayyukan su.

Maaikatan jarida a jamhuriyar Niger sun koka akan yadda suka ce jamiaan tsaro na takura masu a lokacin da suke gudanar da ayyukan su.

Lamari na bayan-bayan nan ko ya faru ne a makarantar Lise Isah Korombe, inda aka tura jamiaan tsaro su murkushe wata zanga-zangar da dalibai zasu yi.

A wannan makarantar ce jamian tsaron suka kwace kamarorin gidan talabijin na TV LABARI,da TV TENERE,bayan da suka lura cewa 'yanjaridar sun nadi dukkan abubuwan da suka faru.

Sai dai daga baya an mayarwa wadannan jarida da kayayyakin su da aka kwace amma sunceba zasu karba basai gaban wasu shaedu, domin idan sun lalata musu kayan aiki sai su san yadda zasu yi.

Hassan Sale Mustafa na cikin shugabannin tashar TV Labari mai zaman kanta yayi wa Sule mumuni Barma Karin bayani.

Ga Sule Mummuni Barma da cikakken rahoton.3’16

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:16 0:00

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG