Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo ta ba da sanarwar kafa gwamnatin hadin gwiwa.
Wannan sanarwar na zuwa ne watanni takwas bayan da Shugaba, Felix Tshisekedi, ya ci zaben Shugaban kasar, wanda aka jinkirta na lokaci mai tsawo.
“A karshe dai an samu gwamnati,” abin da Firaminista, Sylvestre Ilunga Ilukamba, ya fada kenan jiya Litini.
Ya kara da cewa, “Shugaban kasa ya rattaba hannu kan dokar, kuma kwanan nan za mu fara aiki.”
A karkashin yarjajjeniyar raba madafun iko, za a bai wa jam’iyyar DC ta su Tshisekedi mukamai 23, a yayin da kuma mukamai 42 za a bai wa mambobin jam’iyyar su tsohon Shugaban kasar, Joseph Kabila, ta CFC.
Za ku iya son wannan ma
-
Janairu 27, 2023
An Samu Take Hakkin Dan Adam Da Dama a Jamhuriyar Nijar - Rahoto
-
Janairu 25, 2023
Ma’aikatan Kasar Nijar Sun Fara Yajin Aiki Na Wuni Biyu
-
Janairu 25, 2023
Dalilin Da Yasa Amurkawa Bakaken Fata Ke Kaura Zuwa Ghana
Facebook Forum