Yau Litinin an shiga rana ta 31 da rufe wasu ma’aikatun gwamnatin Amurka, a yayin da kuma Shugaban Majalisar Dattawa dan Republican ke shirya yadda za a kada kuri’a, kan wata shawara da Shugaba Donald Trump ya gabatar ta a daidaita, amma kuma shugabannin Dimokarat ke cewa ba ta ma taso ba.
Tsarin da Trump ya yi tayinsa, ya tanadi kariya ga dubban bakin hauren da aka shigo da su cikin Amurka tun suna kanana, da kuma tsawaita wa’adin kare mutanen da su ka guje ma kasashensu saboda tashin hankali ko wani bala’i. A madadin haka kuma a samar da kudi dala biliyan 5.7 don gina katanga akan iyakar Amurka da Mexico.
‘Yan Dimokarat dai na adawa da batun gina katangar da cewa akwai tsada, gashi kuma ba matakin tsaro ne mai inganci ba. Su na bukatar Trump da ‘yan Republican su bude harkokin gwamnati duka kafin a tattauna kan wasu matakan kare kan iyaka.
Shugaban masu rinjaye na Majalisar Dattawa, dan Republican Mitch McConnell ya ce zai gabatar da tsarin da Trump ya yi tayinsa din, don kada kuri’a a kai.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 04, 2023
Amurka Ta Kakkabo Babban Balan-Balan Na Leken Asirin China
-
Janairu 25, 2023
Mawakiya Yar Najeriya Ta Yi Tarihi A Bikin Bada Lambar Yabo Na Oscar
-
Janairu 13, 2023
Lisa Marie Presley, Diyar Mawaki Elvis Ta Rasu
-
Janairu 11, 2023
Ana Tsaftace Yankunan Da Mahaukaciyar Guguwa Ta Ratsa A California
Facebook Forum