Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Tsananta Zanga-zangar Kiran Shugaba Boutlefika Ya Tafi


Cincirindon masu zanga-zanga a Aljeriya
Cincirindon masu zanga-zanga a Aljeriya

Duk da sassautowar da Shugaban Aljeriya ya yi kan sha'awar shugabanci na mutu-ka-raba, 'masu zanga-zangar bukatar ya je ya hutu ba su gamsu da alkawarin da ya yi na rage tsawon wa'adinsa ba.

Masu zanga zangar adawa da gwamnati a kasar Algeria, sun yi biris da alkawarin da shugaban kasar Abdelaziz Bouteflika ya yi, na cewa zai yi dan takaitaccen wa’adi ne, idan aka sake zaben shi a watan Afrilu.

A jiya Litinin, an yi ta zanga, wacce matasa suka jagoranta, tare da kauracewa ajujuwansu na jami’o’i a Algiers, babban birnin kasar.
Sabuwar zanga zangar ta barke ne sa’a guda bayan da ofishin shugaban kasar ya mika takardunsa na neman yin takarar neman wa’adi na biyar a zaben da za a yi a watan gobe.

A Faransa ma, ‘yan kasar ta Algeriya, sun gudanar da zanga zanga, inda akalla mutum dubu shida suka yi gangami a wani dandali da ke birnin Paris a ranar Lahadi, inda suka yi ta furta kalaman batanci akan shugaba Bouteflika mai shekaru 82, wanda ke fama da rashin lafiya, tun bayan da ya samu matsalar shanyewar barin jikinsa a shekarar 2013.

Facebook Forum

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG