Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Tura Jiragen Yaki Jihar Filato


jirgin yaki mai saukar angulu kirar Mi-35P
jirgin yaki mai saukar angulu kirar Mi-35P

Rundunar sojin saman Najeriya ta aika da jirgin yaki mai saukar ungulu Mi-35P da kuma wani mai sa ido da kuma samar da bayanai ISR, a wani yunkurin shawo kan rikicin da ya barke a jihar Filato.

A wata sanarwar da jami’I mai hulda da jama’a na rundunar sojin ya fitar, jiragen za su taimakawa ayyukan da sojojin kasa ke yi a jihar.

Haka zalika, rundunar ‘yan sandan Najeriya ita ma ta aika da dakaru na musamman karkashin jagorancin mataimakin sufeto janar na ‘yan sanda mai kula da ayyuka wanzar da zaman lafiya a jihar.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya, ACP Jimoh Moshood ne ya bayyana hakan yau Litinin inda ya ce dakarun za su je aikin wanzar da zaman lafiya garin barikin-Ladi, da Riyon, da kananan hukumomin kudancin Jos inda jama’a da dama suka rasa rayukansu a karshen makon da ya wuce.

Haka kuma za su je da jirgi mai saukar ungulu guda biyu, da tankoki biyar da ‘yan sandan ko ta kwana da sauransu.

A karshen makon da ya gabata ne rikici tsakanin manoma da makiyaya a Barikin Ladi ya yi sanadin mutuwar mutane 86. Shugaba Buhari ya yi tur da asarar rayukan, da kuma zargin 'yan siyasa da rura wutar rikicin.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG