Harbe-harben bindigogi da aka ji jiya Talata a Khartoum babban birnin kasar Sudan, a lokacin da fada ya kaure tsakanin bangarori daban daban na rundunar sojojin kasar, sun bayyana raunin gwamnatin hadin gwiwar kasar.
Mai magana da yawun gwamnatin Faisal Mohamed Salih ya dora alhakin tashin hankalin a kan Hukumar Leken Asiri da Tsaro ta Kasar da ake kira NISS a takaice, wadda a baya ke goyon bayan tsohon shugaban kasar Omar al-Bashir, da aka hambarar da gwamnatinsa a wani juyin mulki da aka yi a watan Afrilun da ya gabata, bayan an shafe watanni ana zanga-zangar kin jinin gwamnati a kasar.
An mayar da hukumar ta NISS saniyar ware, tun bayan da aka hambarar da gwamnatin tsohon shugaban, yayinda da sojojin Sudan da kuma wasu kungiyoyin mayaka da ake kira Rapid Support Forces da turanci suka zama kungiyoyin mayaka masu karfi na kasar.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 16, 2021
Kungiyar WTO Ta Gabatar Da Sabuwar Shugaba Ngozi Okonjo-Iweala
-
Fabrairu 16, 2021
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) Ta Aminta Da Riga Kafin AstraZeneca
Facebook Forum