Wata babbar jami’ar kwamitin kare hakkin bil’adama na Majalisar Dinkin Duniya dake gudanar da bincike a kasar Myanmar, tace ba mamaki “sojoji sun take haddin bil’adama” a yammacin kasar, da sunan cewa wai suna kokarin rufe kafofin sadarwar Internet.
A jiya Litinin ne Yanghee Lee, ta rubutawa hukumar kare hakkin bil’adama ta Majalisar Dinkin Duniya, cewar an rufe duk wasu hanyoyin sadarwar internet a garuruwan Rakhine dake makoftaka da jihar Chin, yankin da sojoji ke yaki da ‘yan ta’adda na kungiyar Arakan tun a shekarar da ta gabata.
Lee, ta kara da cewar taji kishin-kishin cewar sojoji na binciken harkokin da suka shafi yanar gizo a yankin, wanda hakan na iya zama hanyar muzgunawa fararen hula a yankin.
Kamfanin sadarwa na Telenor Group yace an dakatar da yanar gizo ne a yankin, bisa umurnin ma’aikatar sufuri da sadarwa, bisa dalilin cewar ana amfani da yanar gizon wajen aikata wasu miyagun ayyuka.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 04, 2023
Amurka Ta Kakkabo Babban Balan-Balan Na Leken Asirin China
-
Janairu 31, 2023
Fafaroma Francis Ya Kai Sakon Zaman Lafiya A Afirka Ta Tsakiya
-
Janairu 30, 2023
Mutane 88 Sun Mutu A Wani Harin Bomb A Pakistan
Facebook Forum