Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana Kada Kuri'ar Raba Gardama Kan Sabon Kundin Tsarin Mulki A Zimbabwe


Jama'a sun yi layi a runfunan zabe a kasar Zimbabwe
Jama'a sun yi layi a runfunan zabe a kasar Zimbabwe
‘Yan kasar Zimbabwe suna kada kuri’ar raba gardama kan sabon kundin tsarin mulkin kasar, wanda karon farko zai rage karfin ikon shugaban kasa.

Sabon kundin tsarin mulkin zai takaita wa’adin mulkin shugaban kasa zuwa wa’adin mulkin biyu na tsawon shekaru biyar biyar kawai.

Shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe dan shekaru tamanin da tara, ya shugabanci kasar na tsawon sama da shekaru talatin, kuma ko a karkashin sabon kundin tsarin mulkin ma, zai iya ci gaba da mulki na tsawon shekaru goma.
Mr. Mugabe da abokin hamayyarsa Morgan Tsvangirai, dukansu sun goyi bayan daftarin kundin tsarin mulkin, kuma ana kyautata zaton zai sami gaggarumin goyon baya.

Mutanen biyu sun tsaida yarjejeniyar raba daunin ikon mulkin Zimbabwe bayan kazamin tashin hankalin da ya biyo bayan zaben shekara ta dubu biyu da takwas, sai dai har yanzu suna yiwa juna kallon hadarin kaka. An yi tashin hankali a wurare dabam dabam kafin fara zaben raba gardaman na yau asabar.
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG