Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana Kai Ruwa Rana Tsakanin Gwamnatin Nasarawa Da Kungiyar Kwadago


Wani taro da gwamnatin jihar Nasarawa ta yi da kungiyar kwadago (Hotuna: Usman Tanko/ Nasarawa State Govt)
Wani taro da gwamnatin jihar Nasarawa ta yi da kungiyar kwadago (Hotuna: Usman Tanko/ Nasarawa State Govt)

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya ki amincewa ya sanya hannu kan yarjejeniya da kungiyar kwadago dake yajin aiki saboda janyewa da gamayyar kungiyoyin ma’aikatan jinya a jihar ta yi daga yarjejeniyar.

Shugaban kungiyar kwadago a jihar Nasarawa, Yusuf Sarki Iya ya ce tun farko sun shiga yajin aikin ne saboda gwamnati ta kasa biya masu bukatunsu.

A cewarsa, bukatun sun hada da karin girma ga ma’aikata, rashin bada zarafin kara samun horo wa ma’aikata, rashin biyan karancin albashi na naira dubu talatin da gwamnatin tarayya ta amince da sauransu.

Mai magana da yawun gamayyan kungiyoyin ma’aikatan jinya a jahar Nasarawa, Kyari Caleb ya ce sun lura cewa yarjejeniyar da aka cimma ba ta magance bukatun da suka gabatar ba don haka za su ci gaba da yajin aiki.

Gwamna Abdullahi Sule (Hoto: Usman Tanko/ Nasarawa Government)
Gwamna Abdullahi Sule (Hoto: Usman Tanko/ Nasarawa Government)

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya ce ba zai sa hannu don amincewa da yarjejeniyar ta kungiyar kwadago ba har sai sun sasanta da kungiyar gamayyan kungiyoyin ma’aikatan jinya a jihar.

Yajin aiki da ma’aikata kan shiga a Najeriya, kan zama masu makami wajen neman a biya masu bukatunsu.

Gwamnatoci a lokuta da dam akan zargin ma’aikatan da shiga yajin aikin don cimma burinsu ba tare da suna la’akkari da kuncin da za su jefa al’uma ba.

Saurari cikakken rahoton Zainab Babaji:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:10 0:00


XS
SM
MD
LG