Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

AREWA A YAU: Bunkasa Harkokin Ilimi A Yankin Arewacin Najeriya, Fabrairu 08, 2023


Nasiru Adamu El-Hikaya: Kan Hanyar Kaduna Zuwa Abuja
Nasiru Adamu El-Hikaya: Kan Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

A cikin shirin na wannan makon, mun duba batun bunkasa harkokin ilimi a yankin Arewacin Najeriya, inda yara kanana da dama ba sa zuwa makaranta ko kuma su na gararamba kan tituna ba tare da samun kulawar da ta dace daga gwamnatoci da kuma iyaye ba.

ABUJA, NIGERIA - Akwai matukar bukatar daukar matakan kawo wa irin wadannan yara daukin da zai ceto rayuwarsu ta nan gaba. Za a iya cimma wannan buri ne ta hanyar gudunmawa asusun raya ilimi da tallafi daga hukumomin taimako.

Bincike ya nuna cewa akwai fiye da yara miliyan 10 da ke gallafiri a titunan Arewacin kasar ba tare da samun ilimi ko damar shiga makaranta ba. Tsarin hada makarantun tsangaya da na boko zai yi matukar tasiri wajen magance wannan kalubalen.

Almajiri School
Almajiri School

Shiga shafin a saurari cikakken rahoton:

AREWA A YAU: Bunkasa Harkokin Ilimi A Yankin Arewacin Najeriya, Fabrairu 08, 2023.mp3
please wait

No media source currently available

0:00 0:09:43 0:00

XS
SM
MD
LG