Zaha mai shekaru 28 da haihuwa, ya fadawa kafar yada labarai ta BBC cewa wannan durkuson tamkar wani "kaskanci" ne, a inda ya kamata a ce suna tsaye kaimun domin kare kima da martabar bakaken fata.
Hukumar shirya gasar Premier ta Ingila, na daga cikin hukumomin da suka tsara ‘yan wasa su rika gurfanawa a kan gwiwar kafar su, domin nuna goyon baya ga fafutukar nan ta ‘Black Lives Matter’ wadda aka soma tun bayan mutuwar Ba’amurke George Floyd, sakamakon danne masa wuya da wani dan sanda farar fata yayi.
Zaha ya ce wannan “tamkar muna ware kan mu ne bisa wani tsari da bai da amfani.”
A makon jiya ma Zaha ya saka ayar tambaya akan makasudin gurfanawa da ‘yan wasa suke yi a gwiwar kafar su kafin soma wasa.
Ya ce “ina dalilin cewa har sai mun laka tambarin Black Lives Matter a rigunanmu, domin mu nuna cewa mu (bakaken fata) muna da muhimmanci? Wannan kaskanci ne da faduwar girma.”
Da yake jawabi a wani taron bunkasa kasuwanci a sha’anin kwallon kafa, Zaha ya ce iyayensa sun tarbiyyantar da shi akan alfahari da kasancewarsa bakar fata, don haka zai tsayu ne kaimun akan haka, ba wai durkusawa ba.
Ya kara da cewa ya gaji da yadda ake amfani da shi a matsayin wata kafa ta yaki da wariyar launin fata, wanda ya kamata a dauki kwararan matakai na kawar da shi a duniya.
A wannan makon kuma kungiyar Brentford ta ce ‘yan wasan ta za su daina yin gurfanin kafin wasa, saboda suna ganin cewa yin hakan a yanzu bai da wani tasiri a fafutukar yaki da nuna wariya.