Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ba Zan Koma Kungiyar Gwamnoni Ba Sai An Bayyana Gaskiyar Matsayinmu-Isa Yuguda


Shugaban Kasar Najeriya Goodluck Jonathan yana gabatar da rahoton aikin da gwamnatinsa ta gudanar cikin shekaru biyu
Shugaban Kasar Najeriya Goodluck Jonathan yana gabatar da rahoton aikin da gwamnatinsa ta gudanar cikin shekaru biyu

Gwamnan jihar Bauchi Isa Yuguda yace ba zai koma kungiyar gwamnoni ba sai an fayyacewa 'yan Najeriya gaskiyar matsayin gwamnonin arewacin kasar kan zaben shugaban kungiyar gwamnoni

Gwamnan jihar Bauchi Isa Yuguda ya bayyana dalilinsa na janye jiki daga kungiyar gwamnonin kasar.

A cikin hirarshi da manema labarai gwamna Yuguda ya bayyana cewa, gwamnonin arewacin Najeriya goma sha tara sun amince su tsaida gwamnan jihar Plateau Jonah Jang a matsayin wanda zai gaji gwamna Rotimi Amechi na jihar Rivers a matsayin shugaban kungiyar gwamnonin.

Bisa ga cewar gwamna Yuguda, tsarin kungiyar bai bada damar shugabantar kungiyar karo na biyu ba. Ya bayyana cewa, hakin shugaban kungiyar gwamnonin arewacin Najeriya ne, ya fita fili ya fayyacewa ‘yan Najeriya gaskiyar matsayinsu a kan wanda suka tsayar ya wakilcesu ba tare da hamayya ba, abinda yace ya basu damar tsaida shugaba sabili da sune suke da rinjaye.

Da yake amsa tambayoyin wakilinmu Abdulwahab Mohammed, gwamna Isa Yuguda, yace hakin al’ummar jihar da suka zabe shi yasa ya zama tilas ya tsaya kan gaskiya domin kare mutumcinsu.
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:35 0:00
Shiga Kai Tsaye
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG