Gwamnan jihar Bauchi Isa Yuguda ya bayyana dalilinsa na janye jiki daga kungiyar gwamnonin kasar.
A cikin hirarshi da manema labarai gwamna Yuguda ya bayyana cewa, gwamnonin arewacin Najeriya goma sha tara sun amince su tsaida gwamnan jihar Plateau Jonah Jang a matsayin wanda zai gaji gwamna Rotimi Amechi na jihar Rivers a matsayin shugaban kungiyar gwamnonin.
Bisa ga cewar gwamna Yuguda, tsarin kungiyar bai bada damar shugabantar kungiyar karo na biyu ba. Ya bayyana cewa, hakin shugaban kungiyar gwamnonin arewacin Najeriya ne, ya fita fili ya fayyacewa ‘yan Najeriya gaskiyar matsayinsu a kan wanda suka tsayar ya wakilcesu ba tare da hamayya ba, abinda yace ya basu damar tsaida shugaba sabili da sune suke da rinjaye.
Da yake amsa tambayoyin wakilinmu Abdulwahab Mohammed, gwamna Isa Yuguda, yace hakin al’ummar jihar da suka zabe shi yasa ya zama tilas ya tsaya kan gaskiya domin kare mutumcinsu.
A cikin hirarshi da manema labarai gwamna Yuguda ya bayyana cewa, gwamnonin arewacin Najeriya goma sha tara sun amince su tsaida gwamnan jihar Plateau Jonah Jang a matsayin wanda zai gaji gwamna Rotimi Amechi na jihar Rivers a matsayin shugaban kungiyar gwamnonin.
Bisa ga cewar gwamna Yuguda, tsarin kungiyar bai bada damar shugabantar kungiyar karo na biyu ba. Ya bayyana cewa, hakin shugaban kungiyar gwamnonin arewacin Najeriya ne, ya fita fili ya fayyacewa ‘yan Najeriya gaskiyar matsayinsu a kan wanda suka tsayar ya wakilcesu ba tare da hamayya ba, abinda yace ya basu damar tsaida shugaba sabili da sune suke da rinjaye.
Da yake amsa tambayoyin wakilinmu Abdulwahab Mohammed, gwamna Isa Yuguda, yace hakin al’ummar jihar da suka zabe shi yasa ya zama tilas ya tsaya kan gaskiya domin kare mutumcinsu.