Bankin Duniya ya kaddamar da shirin farfado da matsayin ilmin yara da ya lalace a jihar Bauchi, a sanadiyar rashin kai yara makaranta domin samun ilmi, wanda a halin yanzu bincike ya nuna cewar akwai yara da basa zuwa makaranta su fiye da miliyan 1 a jihar.
A matakin farko domin cimma manufar shirin, Bankin Duniyar ya zabo malamai gogaggu su 60, domin koya musu wasu dabarun cusa ilimi, wanda za suje makarantu domin su koyar da malaman makarantu dake yankunan kananan hukumomin jihar.
Hukumar samar da ilmi ta kasa a matakin jiha ita ce ke sa ido wajen tafiyar da wannan shirin.
Sai dai kuma matsalar ta karu da rashin kai yara makaranta da iyaye basa yi domin rashin abin hannu, da kuma sakaci. Amma wakilin Muryar Amurka ya tuntubi Malam Nuru Ahmed Daraktan tsare tsare a hukumar samar da ilmi na jiha, domin jin matakan da ake dauka da hukunci don magance matsalar.
Ga rahoto a sauti daga wakilin Muryar Amurka Abdulwahab Muhammad.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 27, 2021
Lokacin Lallashin Masu Daukar Makami Ya Wuce- Buhari
-
Fabrairu 27, 2021
An Saki 'Yan Makarantar Kagara Da Malamansu
-
Fabrairu 27, 2021
Kayan Masarufu Sun Yi Tashin Gwauron Zabi A Kudancin Najeriya
-
Fabrairu 27, 2021
'Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 6 Tare Da Sace Wasu 15 A Jihar Neja
-
Fabrairu 27, 2021
Ana Zargin DSS Da Kama Salihu Tanko-Yakasai Bayan Sukar Buhari
Facebook Forum