Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Brazil na Shakkar Kamaru


A wani lamari mai ban dariya, kungiyar kwallon kafar kasar Brazil

A wani lamari mai ban dariya, kungiyar kwallon kafar kasar Brazil, wadda aikin dake gabanta, na zuwa zagaye na biyu a gasar da take saukar bakinta, bashi da wani wahala ne, kawai kunnen doki zatayi da Kamaru, ko kuma ta ma bubbuge Kamarun, kasar dake haramar tafiya gida bayan kammala wasanta na karshe da Brazil din.

Amma a wannan gasa dake cike da abubuwan ban mamaki, Brazil dai ta fara shakkar Kamaru, kafin wasan da za’a yi ran Litinin dinnan mai zuwa a birnin Brasilia.

‘Yan wasan Brazil din sunyi ammana cewa yin wasa da kungiyar da bata da wani abun rashi, wahalar wasan zai iya fin yadda ake zato.

“Zamu yi arangama ne da kungiyar da bata da wani abun da zata rasa,”, dawan wasan bayan Brazil David Luiz yace. “’Yan wasansu zasu yi kokarin nuna cewa zasu iya yin wasan da yafi wasanni biyu da suka yi a baya. Cinye mai masaukin baki zai zaman musu kamar cin kofin ne baki daya.”

Brazil dai yanzu itace a saman rukunin group G da maki 4.
please wait

No media source currently available

0:00 0:04:00 0:00
Shiga Kai Tsaye
XS
SM
MD
LG