Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Buhari Ya Bukaci Zaman Lafiya A Najeriya A Sakon Sa Na Kirsimeti


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, a sakon shi na taya al'ummar Kirista murnar bikin Kirsimeti, wanda ya isar ta bakin kakakin sa, Malam Garba Shehu a jiya Laraba, ya yi kira ga duk masu tada zaune tsaye da su zauna lafiya da sauran al'ummar kasar.

Reverend Dakta Zacharia Samjumi shine babban sakataren sakateriyar darikar Katolika ta kasa, ya bayyana cewa Kirsimeti lokacine na sulhu, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su zauna lafiya da juna.

Wasu daga cikin ‘yan Najeriya kamar Mista Onyebueke Ike ya nuna farin cikin sa, kuma yana taya ‘yan Najeriya murnar bikin Kirsimeti. “Amaka Iroegbute da Ezealor Daniel cewa suka yi suna nuna farin cikin da Allah Ya kawo su wannan rana ta Kirsimeti, kuna suna kira ga ‘yan Najeriya da su zauna lafiya da kaunar juna.”

Saurari rohoton Wakilin Muryar Amurka, Alphonsus Okoroigwe, a cikin Sauti.


Facebook Forum

XS
SM
MD
LG