Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Buhari Ya Tsawata Wa Shugabannin Tsaro


Shugaba Muhammadu Buhari
Shugaba Muhammadu Buhari

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya soki shugabbanin tsaro bisa yadda suke aiwatar da ayyukansu, ganin yadda ake ta kai hare-hare a arewacin Najeriya.

A cewar shugaban, dole sai an kara kokarin da ake yi wajen kawo karshen matsalar rashin tsaro da ake fuskanta a kasar.

Babban mai bai wa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Babagana Monguno ne ya bayyana kalaman shugaban jim kadan bayan da Buhari ya gana da shugabbanin na tsaro a yau Alhamis.

Wadannan kalaman na shugaban sun kasance kalamai mafiya kaushi game da salon shugabbanin na tsaro a arewacin Najeriya, a daidai lokacin da yanayin tsaro ke kara muni.

A cewar Mongonu shugaban Najeriya ya nuna matukar damuwa kan yadda matsalar tsaro ke kara muni a kasar.

“Shugaban kasar yana ganin duk da cewar hukumomin tsaro na kokari, kokarin nasu bai isa ba wajen cimma burinsu cikin gaggawa,” a cewar Mongonu.

Tun a shekarar 2015 ne aka samu kau da Boko Haram daga yawancin yankunan da ta mamaye amma duk da hakan kungiyar ta ci gaba da kai hare-hare a arewa maso gabashin Najeriya da kasashen Nijar da Kamaru.

A ranar Lahadi ma wasu mayaka sun kashe akalla mutum 60 a Borno, kwanaki kadan aka sake kai wani hari a yankin, inda mutum 69 suka rasa rayukansu.

A cikin watan Mayu, Majalisar Dinkin Duniya ta ce tashin hankali ya sa mutum 23,000 sun gudu daga Najeriya zuwa Nijar cikin mako daya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG