A yau Litinin, Jami'an kiwon lafiya a China, sun tabbatar da cewa, adadin mutanen da suka kamu da cutar Coronavirus, ya zarce dubu saba'in, yayin da addadin wadanda suka mutu kuma, ya doshi kusan mutum 1,800.
Amma kimanin mutune dubu 11,000, da suka kamu da cutar sun warke.
Hukumomi a Lardin Hubei, na kasar China, inda cutar ta samo asali, sun ce, a yau Litinin, an samu karin mutum 100, da suka mutu, sanadiyyar cutar, yayin da karin wasu ma'aikatan lafiya suka isa yankin, don taimakawa fannin kiwon lafiyar da ya shiga wani hali tun bayan barkewar cutar a watan Disamba.
An dai tabo batun wannan babbar barazana, da cutar ta Coronanavirus, ke yi wa duniya, a babban taron tsaro, na kasa da kasa, da ake yi, a birnin Munich, da ke Jamus, inda shugaban hukumar Lafiya ta duniya (WHO) Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya yi tsokaci.
Ya ce, “Duniya na kashe biliyoyin daloli wajen yin shirin tunkarar hare-haren ta’addanci, amma, ba a kyakkyawan shiri kan barkewar wata cuta, wanda hakan hadari ne da zai shafi rayuka, tattalin arziki, siyasa, da al’amuran yau da kullum.”
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 16, 2021
Kungiyar WTO Ta Gabatar Da Sabuwar Shugaba Ngozi Okonjo-Iweala
-
Fabrairu 16, 2021
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) Ta Aminta Da Riga Kafin AstraZeneca
Facebook Forum