A yau lahadi, cutar Coronavirus mai saurin kisai, ta halaka mutum na farko a wajen kasar China inda cutar ta samo asali.
Lamarin ya faru ne a kasar Philippines.
Jami’an kiwon lafiya a tsakiyar Lardin Hubei, inda cutar ta barke, sun ce mutum 304 ne suka mutu ya zuwa yanzu a China, sannan wasu dubu 14 suke dauke da ita.
Tun a makonnin da suka gabata aka garkame birnin Wuhan a lardin Hubei, amma jami’ai har ila yau sun ce an rufe birnin Wenzhou ma a yau Lahadi.
Wenzhua na da tazarar kilomita 800 tsakaninsa da Wuhan.
Rahotanni sun nuna cewa wasu mazauna birnin na Wuhan sun yi zargin cewa an yi rufa-rufa tun farkon bullar cutar, ciki har da mazauna yankin da likitoci.
Bayanai sun yi nuni da cewa, yin magana kan cutar wacce ta bulla a watan Disamba, kan sa jami’an gwamnati su yi wa mutum barazana a wasu lokuta ma har da tsarewa.
“Tuni rade-radin wannan lamari ya fantsama a shafukan intanet,” in ji Flora Fauna, Ba’amukiya ‘yar asalin yankin Wuhan wacce ta boye sunanta yayin wata ganawa da ta yi da Sashen Mandarin na VOA.
“Maimakon a dauki matakan da suka dace, sai gwamnatin birnin ta turo ‘yan sanda suna kama mutanen da ke yada labaran,” a cewar Fauna.
Za ku iya son wannan ma
-
Fabrairu 18, 2021
Kungiyar Kasuwanci ta Duniya Na Bukatar Sabon Salon Gudanarwa-Dr. Ngozi
-
Fabrairu 18, 2021
Guterres Ya Yi Kiran a Samar Da Tsarin Bai Daya Na Rigakafin Coronavirus
-
Fabrairu 16, 2021
Kungiyar WTO Ta Gabatar Da Sabuwar Shugaba Ngozi Okonjo-Iweala
-
Fabrairu 16, 2021
Hukumar Lafiya Ta Duniya (WHO) Ta Aminta Da Riga Kafin AstraZeneca