Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

COVID-19 Ta Kashe Wani Babban Dan Siyasa a Congo


Wani babban dan siyasa a Congo wanda jigo ne a bangare ‘yan adawa ya rasu sanadiyyar cutar COVID-19.

Kafafen yada labaran kasar ta DRC, sun ruwaito cewa iyalan Pierre Lumbi ne suka bayyana mutuwarsa a Kinshasa a jiya Lahadi, sai dai ba a san ainihin shekarunsa ba.

Mamacin shi ne shugaban gangamin yakin neman zabe na madugun ‘yan adawa Martin Fayulu a lokacin ya ya tsaya takarar neman shugabancin kasar ta Congo a shekarar 2018.

A wani labari makamncin wannan kuma, shugaban Ghana Nana Akufor Addo, ya sanar da cewa ministan lafiyar kasar Kwaku Agyeman Manu ya kamu da cutar ta coronavirus amma kuma yana cikin yanayi na koshin lafiiya.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG