Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

COVID-19: ‘Yan Afghanistan Da Yawa Sun Bar Iran Zuwa Kasarsu


Wani rahoton kamfanin dillancin labaran Associate Press (AP) ya bayyana cewa akalla ‘yan kasar Afghanistan mazauna Iran 200,000 suka koma gida a ‘yan makonnin nan sakamakon annobar cutar coronavirus (COVID-19) a Iran.

Rahoton ya ce ‘yan Afghanistan mazauna Iran suna ficewa ne daga kasar da take daya daga cikin kasashen duniya da annobar ta fi kamari, zuwa kasarsu ta asali wadda ita kuma bata yi wani tanadi na shirin yakar cutar ba.

‘Yan Afghanistan suna komawa kasarsu ba tare da an gwada ko suna dauke da cutar ba ko a'a. Kamfanin dillancin labaran na AP ya kuma ce mutanen dake komawa suna iya zama sanadin samun barkewar annobar a kasar, lamarin da zai iya fin karfin asibitocin dake kasar.

Jami’an Afghanistan sun ce suna fargabar Iran zata tilasta fitar da ‘yan Afghanistan kusan miliyan daya daga Iran.

Kungiyar kasa-da-kasa ta ‘yan gudun hijira ta ce fiye da ‘yan Afghanistan 145,000 ne suka koma gida a watan jiya, saboda barkewar annobar coronavirus.

Iran na da mutane sama da 58,000 da suka kamu da cutar coronavirus, a Afghanistan kuma mutun 367 kacal, a cewar tsangayar binciken annobar COVID-19 ta jami’ar Johns Hopkins.

  • 16x9 Image

    Yusuf Harande

    Yusuf Aliyu Harande, dan jarida da ke aiki da Sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA). Yana da kwarewa a fannoni da dama, da suka hada da shafukan yanar gizo, talabijin, bincike, rubutu da hotuna. Dan asalin kauyen Hiliya ne daga karamar Hukumar Tambuwar a jihar Sakkwato.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG