Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

COVID: An Soke Lasisin Wata Makaranta a Kaduna Bisa Keta Dokar Killacewa


Hoton sanarwar soke lasisin makarantar
Hoton sanarwar soke lasisin makarantar

Gwamnatin jihar Kaduna ta rufe makarantar Leaders International School bayan da ta keta dokar killacewa wadda aka kafa domin takaita yaduwar cutar Coronavirus.

Ta kuma soke lasisin makarantar a cewar wata sanarwar da ma'aikatar ilimi a jihar ta fitar.

Makarantar ta keta dokar da aka kakaba a jihar wacce ta umarci dukkanin makarantu su kasance a garkame har sai an tsai da shawara kan lokacin da ya kamata a bude su.

A cewar sanarwar, makarantar ta gudanar da jarabawar shiga ajin JSS1 da SS1 a jiya, 10 ga watan Yuni cikin harabar makarantar.

Bancin rufe makarantar da aka yi, za a kuma hukunta mai makarantar.

Tun ranar 23 ga watan Maris ne dai aka rufe makarantu a jihar Kaduna, kuma ma'aikatar lafiya a jihar ta jadadda muhimmancin mayar da hankali kan karatu ta yanar gizo.

A cikin makon nan ne Gwamnan Nijar Kaduna, Nasir El-Rufai ya dage dokar zama a gida, tare da kuma bude wasu fannoni na kasuwanci da rayuwa a jihar.

Amma duk da haka, gwamnan ya bayyana cewa dole ne makarantu su kasance a rufe, sai masu ruwa da tsaki sun yanke shawara kan lokacin da ya kamata a bude su.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG