Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Cutar Ebola Ta Sake Kashe Wani A Kasar Congo


Wani Malami na amfani da na’urar auna zafin jiki domin neman alamun cutar Ebola.
Wani Malami na amfani da na’urar auna zafin jiki domin neman alamun cutar Ebola.

Ma’aikatar lafiya ta kasar Congo ta sanar da mutuwar wani kuma yau lahadi wanda ya kamu da cutar Ebola.

An sami Karin wadansu mutane hudu da suke dauke da kwayar cutar ta Ebola a damokaradiyar jamhuriyar Kwango, bisa ga cewar ma’aikatar lafiyar a sanarwar da ta fitar ta baya bayan nan.

Kawo yanzu, an bada rahoton cewa, mutane arba’in da shida suka kamu da zazzabin mai sa zubar jinni tunda aka sami barkewar cutar.

Shugaban kasar Joseph Kabila da majalisarsa sun tsaida shawara jiya asabar su kara yawan kudin da ake kashewa wajen gudanar da agajin gaggawa a kokarin shawo kan cutar Ebola, da zai kai sama da dala miliyan hudu

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG