Bayan da hukumar INEC ta dage zaben gwamnoni da na ‘yan majalisun jiha zuwa 18 ga watan Maris, hukumar kidayar kasa ta nemi gwamnati ta ba ta damar dage kidayar jama’a da gidaje daga ranar 29 ga watan Maris zuwa karshen watan Mayu, a cewar Garba Shehu.
Malam Garba Shehu ya kuma ce majalisar kolin kasar ta amince a ba hukumar kidaya ta kasa makudan kudi, da za a yi amfani da su don sayen wata na’ura da zata taimaka wajen yin kidayar.
Wannan dai shi ne karon farko da za a yi kidaya da fasahar zamani a Najeriya, a cewar Garba Shehu. Ya kara da cewa jami’ai zasu yi amfani da kwamfuta, sannan na’urar zata yi amfani da tauraron dan adam.
A kidayar da aka yi a shekarun baya, an samu korafe-korafe game da sakamakon kidayar, amma a wannan karon ana sa ran sabuwar fasahar zata taimaka wajen kawar da wadannan korafe-korafen.
Garba Shehu ya kuma ce a wannan tsarin, gwamnatin Buhari ba ta bada damar wani yayi amfani da kididdigar ya tada hankali ko kawo wani bambancin kabilanci ko na addini ba.
Nan take dai shugabannin hukumar gudanar da kidaya a karkashin jagorancin Malam Nasiru Isah Kwara, ba su ce komai ba akan batun, sai dai suka ce suna jiran karin bayanai daga fadar shugaban kasa.
Saurari cikakken rahoton Umar Faruk Musa: