Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

David Cameron Zai Yi Murabus Daga Kujerarsa Ta Majalisar Dokoki


Tsohon Farai Ministan Birtaniya David Cameron
Tsohon Farai Ministan Birtaniya David Cameron

Tsohon Firai Ministan Birtaniya David Cameron ya bada sanarwar yin murabus daga kujerarsa ta majalisar dokoki, abin da zai kawo karshen harkokin siyasarsa, makwanni bayan da ya sha kasa a zaben raba gardama na ranar 23 ga watan Yuni na neman zama ko ficewar kasar daga kungiyar Taryyar Turai.

Lokacin da Cameron, dan shekaru 49 da haihuwa, ya gabatar da takardan murabus a matsayin Prime Minstan ya bayyana niyyarsa na ci gaba da zama a majlisar koda yake ba rike shugabancin jami’aiyarsa ta Conservative ba.

Cameron yace ya shaidawa sabuwar Farai Minista Theresa May, cewa zai daina wakiltan mazabarsa a Oxfordshire don ya bada dama ga wani maye gurbinsa akan kujeran, wanda zai mai da hankali a kan yankin dake tsakiyar Ingila.

Sanarwar bazata da Cameron yayi, ana sa ran zai sa a gudanar da zaben cike gurbi na kujeransa ta mazabar Oxfordshire.

Hawan Nasarawa, jihar Kano a Najeriya, lokacin da aka gudanar da bukukuwan Sallar Eid el Fitr
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:44 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG