Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Diego Costa Zai Koma Taka Leda a Brazil


Diego Costa

Tsohon dan wasan Chelsea Diego Costa na shirin kulla yarjejeniyar shekara biyu da kungiyar kwallon kafa ta Palmeiras da ke Brazil, wacce ya kasance yana kauna tun yana yaro.

Hakan na nufin Costa zai koma garinsa na Sao Paulo bayan da ya kwashe shekara 15 yana wasa a nahiyar turai.

Dan shekara 32, Costa wanda ya bar Atletico Madrid a watan Janairu, yana kan tattaunawa da kungiyar ta Palmeiras wacce tana daya daga cikin gaggan kungiyoyin wasan kwallon kafa a Sao Paulo.

Kungiyar ta yi masa tayin kwantiragin shekara biyu kan kudi pam miliyan 2.6 bayan an cire haraji. Rahotanni sun ce yanzu haka dan wasan har ya isa kasar ta Brazil a cewar shafin yanar gizo na Sky Sports.

Baya ga kungiyar ta Palmeiras, akwai kungiyoyin da suke tattauanawa da Costa a Turkiyya, Qatar da Saudiyya tun bayan da ya fice daga Madrid.

Rahotanni sun ce kungiyar Al-Shabab ta Saudiyya ta kusanci kulla yarjejeniya da shi amma ba a samu jituwa ba a karshe.

Hakazalika akwai kungiyoyi a gasar Premier League da suka nuna sha’awar sayensa amma abin ya cutura.

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG