Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

DOMIN IYALI: Ana Zargin Magidanci Da Bata 'Ya'yansa Kanana-Kashi Na Daya.


Grace Alheri Abdu

A shirin Domin Iyali na yau mun yi hira a wata mata a unguwar Rigassa cikin garin Kaduna wadda ta yi zargin mijinta yin lalata da 'ya'yansu mata kanana biyu 'yan shekara shida da kuma uku, batun da kananan yaran suka nanata a hirarraki da aka yi da su, binciken likitoci kuma ya tabbatar.

Sai dai magidancin ya musanta zargin, ya kuma saki matar da yace tana bata mashi suna. Baya ga haka, ya kai kara kotu da nufin neman a kwatar mashi 'ya'yan daga hannun mahaifiyarsu.

Saurari kashin farko na hirar shirin da mahaifiyar yaran.

An Zarfi mahaifi da lalata 'ya'yansa mata PT1-10:00"
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:27 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG