Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

DOMIN IYALI: Matsalar Fyade A Najeriya- Kashi Na Daya, Yuni 11, 2020


Alheri Grace Abdu
Alheri Grace Abdu

Ga wadanda suka jima suna sauraron shirin Domin Iyali, sun sha jin shirin na haska fitila kan matsalar fyade da ake fama da ita a Najeriya. Sai dai, kawo yanzu, hakar shirin bata cimma ruwa ba domin ganin yadda lamarin yake kara ta’azzara musamman a wannan lokacin da aka hana zirga zirga, da ya kai ga mata a sassa dabam dabam na kasar suka shiga zanga zangar kira ga hukumomi da shugabannin al’umma su dauki mataki.

Ta haka, shirin Domin Iyali ya gayyaci ‘yan fafatuka mata da nufin neman hanyar dakile wannan mummunar dabi’a.

Wadanda muka gayyato sun hada da kwamishinar ma’aikatar harkokin mata ta jihar Nassarawa Hajiya Halima jabiru, da Saudatu Mahdi shugabar kungiyar kare hakkokin mata da kananan yara WRAPA, da Hajiya Safiya Adamu, daya daga cikin shugabannin kungiyar dake hankoron kare hakkokin kananan yara da ake kira Tallafi Najeriya, sai kuma Aisha Buba kwararriya a fannin sanin halayyar dan adam.

Saurari kashin farko na tattaunawar da wakiliyar Sashen Hausa, Shamshiya Hamza ta jagoranta.

Matsalar Fyade A Najeriya PT1:10:00"
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:50 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG